Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Sarki Muhammadu Sunusi II ya amsa takardar tuhumar da gwamnatin Kano ke masa

Published

on

Mai martaba sarkin Kano Malam Muhammadu Sanusi ll ya musanta zargin da Hukumar karbar korafi da yaki da cin hanci da rahsawa ta jihar Kano ke masa na barnatar da sama da naira biliyan uku mallakin masarautar Kano.

Wannan na kunshe cikin takardar tuhumar da sarkin ya amsawa gwamnatin jihar Kano, mai dauke da sa hannun mukaddashin sakataren majalisar masarautar Kano Malam Abba Yusuf.

A cewar sarkin lokacin da ya hau karagar mulkin Kano, ya samu naira biliyan daya da miliyan dari takwas da casa’in da uku, da dubu dari uku da talatin da takwas, da dari tara da ashirin da bakwai, da kuma kwabo talatin da takwas a lalitar masarautar.

Mai martaba sarkin Kano ta cikin takardar ya kuma bayyana cewa shi ba jami’in lura da sashen kudi bane, don haka bashi da alhakin yadda za’a sarrafa kudin masarautar Kano.

Idan za a iya tunawa dai a ranar Alhamis din da ta gabata ne gwamnatin jihar Kano ta aikewa Malam Muhammadu Sanusi na biyu takardar tuhumar, kan zargin da ake masa da barnatar da sama da naira biliyan uku mallakin masarautar, tun daga lokacin da ya hau mulki zuwa yanzu.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!