Labarai
Sarkin Kano ya naɗa sabon Dagacin Garun Malam

Mai martaba Sarkin Kano Khalifa Muhammadu Sunusi II, ya hori Sabon Dagacin garin Yada Kwari da ke karamar hukumar garun Malam Alhaji Usman Ibrahim da ya zauna lafiya da jama’ar sa lafiya tare da kula da harkokin ilimi, lafiya da kuma tsaro a yankin nasa.
Sarkin ya kuma umarce shi da ya guji zalunci ko haɗa kai da barayi da ma duk wasu ɓata gari, kana duk lokacin da aka ga bakuwar fuska a sanar da jami’an tsaro.
Khalifa Muhammadu Sunusi II, biyu ya kuma umarci sabon Dagacin, da ya kafa zauren sulhu don sasantawa da dai-daita al’umma.
A nasa jawabin Sabon dagacin garin na Yada Kwari Malam Usman Ibrahim, ya ce, zai yi aikinsa bisa gaskiya da rikon amana kamar yadda ya gada a wajen magabatansa.
You must be logged in to post a comment Login