Labarai
Sauye-sauyen tattalin arzikin da gwamnatina ke aiwatarwa sun jefa talakawa cikin wahala- Shugaba Tinubu

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu, ya ce sauye-sauyen tattalin arzikin da gwamnatinsa ke aiwatarwa sun jawo wa ‘yan Najeriya wahala, yana mai cewa shi ma ya rasa barci da kuzari da ya tilasta masa ramewa da kuma shiga matsananciyar damuwa sakamakon matsin rayuwar da ake ciki.
Shugaban ya bayyana hakan ne yayin karbar tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC domin zaben shekarar 2027.
Tinubu ya ce yana sane da radadin da jama’a ke ciki sakamakon gyare-gyaren tattalin arziki da aka fara tun bayan hawansa mulki, amma ya jaddada cewa dole ne ya ci gaba da aiwatar da su domin gyara kasar.
Tinubu ya lashe zaben fidda gwanin da kuri’u 10,999,162, inda ya kayar da abokin takararsa guda daya, Stanley Osifo, wanda ya samu kuri’u 16,503.
You must be logged in to post a comment Login