Connect with us

Labarai

SERAP ta maka Kamfanin NNPCL a gaban kotu

Published

on

Kungiyar rajin tabbatar da adalci ta SERAP, ta shigar da ƙara a kotu kan Kamfanin man fetur na kasa NNPCL, bisa zargin kasa yin cikakken bayani kan wasu kuɗaɗe da suka kai sama da Naira tiriliyan 211 da aka nuna a cikin rahoton binciken kuɗaɗen kamfanin na shekarar 2023.

 

SERAP ta ce waɗannan kuɗaɗe na cikin rahoton binciken kamfanin na shekarar 2023, a ƙarƙashin rukunin Sauran Kuɗaɗen da ake bin Kamfanin, da kuma Kuɗaɗen da aka tara amma ba a biya ba, ba tare da an yi isasshen bayani da zai ba jama’a damar fahimtar yadda aka gudanar da mu’amalolin ba.

 

Kungiyar ta ce manufar ƙarar ita ce neman kotu ta umarci NNPCL ta bayyana cikakkun bayanai kan waɗannan kuɗaɗe domin tabbatar da gaskiya, riƙon amana da kuma kare dukiyar al’ummar kasar nan. 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!