Labarai
Rundunar Soja ta kama jami’inta da ta ke nema ruwa a jallo

Rundunar Sojin Najeriya, ta sanar da kama wani jami’inta Mohammad Yusuf, wanda ta ayyana nemansa ruwa a jallo bisa zargin safarar kayan aikin soja ga ‘yan ta’adda.
Ta cikin wata sanarwa da ta fitar rundunar ta ce an kama jami’in ne a ranar 25 ga Yuli a tashar Jidari da ke Maiduguri, Jihar Borno, bayan bayanan sirri sun nuna cewa yana ƙoƙarin tsallakawa zuwa ƙasar Kamaru.
A cewar rundunar Operation HADIN KAI, Yusuf wanda ke aiki a Nigerian Army Ordnance Kits Factory da ke Legas, ya tsere daga sansaninsa tun ranar 7 ga Yuli, sannan ya ɓuya a unguwar Gomari Costain da ke ƙaramar hukumar Jere tare.
Ya zuwa yanzu dai ana ci gaba da gudanar da bincike domin gano wadan da ke da hannu a kan lamarin.
You must be logged in to post a comment Login