Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Addini

Shari’ar Abduljabbar: Kotu ta fara sauraron shaidu

Published

on

Babbar Kotun shari’ar musulunci dake zamanta a kofar kudu karkashin mai shari’a Ibrahim Sarki Yola ta fara sauraran shaidun da gwamnatin Kano ke gabatarwa kan sheikh Abduljabbar Kabara.

Lauyan gwamnati Barista Mamman Lawan Yusufari ne ya jagoranci lauyoyin, inda kuma Barista Umar Muhammad ya jagoranci lauyoyin wanda ake kara.

Kotu tayi waiwaye inda ta tambayi lauyoyin Malam Abduljabbar ko suna nan a matsayinsu na kin amincewa da cigaba da shari’a sakamakon lauyoyin baya sunki amincewa da cigaba?

Nan take sabon lauyan yace a cigaba, lamarin da ya sanya aka fara gabatar da shaidu biyu.

An gabatar da shaida na farko mai suna Adam Adam mazaunin filin D.O dake Gwale inda ya ce yana zuwa karatun da ake yi a Masallacin As’habul Kahfi da Jami’atur Rasul dake Sabuwar Gandu.

Kotu tasa shi ya yi rantsuwa, sannan lauyan gwamnati ya fara yi masa tambayoyi, inda ya tabbatar da tuhumar da ake yiwa Malamin.

Haka shima lauyan Malamin ya yi masa tambayoyi, inda aka tafi hutu bayan yimasa tambayoyin za kuma a dora idan an dawo.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!