Labarai
Shettima ya isa Saliyo domin taron shugabannin ECOWAS

Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, ya isa birnin Lungi na kasar Saliyo domin halartar taron shugabannin kasashe da gwamnatocin kungiyar ECOWAS karo na 69.
An tarbe shi a filin jirgin saman Lungi daga cikin jami’an gwamnatin Saliyo da na Najeriya, ciki har da Mataimakin Shugaban Kasar Saliyo, Dr. Mohamed Jalloh, Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Ambasada Bianca Odumegwu-Ojukwu, da wasu manyan jami’an diflomasiyya.
Ana sa ran shugabannin kasashen kungiyar za su tattauna batutuwan da suka shafi zaman lafiya, tsaro, bunkasa tattalin arziki da karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen Yammacin Afirka. Rahoton Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ce halartar Najeriya na nuna kudurin kasar na ci gaba da taka rawa wajen inganta hadin kan kasashen ECOWAS.
You must be logged in to post a comment Login