Labarai
Ganawar Shugaban APC da Sanata Rufai Hanga ta janyo ce-ce-ku-ce

Shugaban Jam’iyyar APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya gana da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, tare da Sanatan Kano ta Tsakiya, Rufai Hanga, a wata ganawa da aka gudanar a boye ranar Lahadi.
A cewar Yilwatda, tattaunawar ta mayar da hankali ne kan hadin kai, zaman lafiya da ci gaban jihar Kano, inda ya ce shugabanni na da alhakin tattaunawa da hada kai domin tabbatar da ci gaban dimokuradiyya da fifita muradun al’umma.
Ganawar na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da sauye-sauyen siyasa gabanin zaben 2027. Sanata Rufai Hanga, wanda ke cikin jagororin NDC a Kano, ya rasa tikitin takarar Sanatan Kano ta Tsakiya bayan jam’iyyar ta bai wa tsohon mataimakin gwamnan Kano, Nasiru Yusuf Gawuna, tikitin takara. Wannan ya kara haifar da rade-radin cewa Hanga na iya sake nazarin makomarsa ta siyasa.
You must be logged in to post a comment Login