Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Shiyyar Kano da kewaye za su amfana da wutar lantarki – KEDCO

Published

on

Kamfanin rarraba hasken lantarki na Kano KEDCO yace abokan huldar sa dake shiyyar Kano da kewayan ta za su fara amfana da karin wutar lantarki bayan da kamfanin ya inganta harkokin sa.

Hakan ya biyo bayan nasarar da kamfanin TCN yayi na kammala gyara a layin samar da wuta na Shiroro-Mando wanda yake samar da wuta ga alummar jihar Kano da kewayen sa.

Wannan na kunshe ne cikin sanarwar da mai magana da yawun kamfanin  na KEDCO Ibrahim Sani Shawai ya sanyawa hannu.

Sakamakon wannan aikin da kamfanin na TCN yayi na kara yawan wutar da yake samar wa daga karfin MW 150 zuwa MW 200 a kullum kuma hakan zai cigaba in dai har ana samun cigaba daga tashar wutar.

Labarai masu alaka :

Kungiyar ma’aikatan lantarki sun garkame ofishin KEDCO

Kungiyar ma’aikatan lantarki ta janye yajin aikin data tsuduma

Kamfanin TCN ta tallata gwanjon jirage masu saukar ungulu

Akan haka ne Kamfanina KEDCO yake yabawa abokan huldar sa saboda kyaky-kyawar fahimtar da suka yi, yayin da suka bukaci kwastomin su kan su ci gaba da biyan kudin wuta akan lokacin mussaman ma a shiyar Kano da Katsina da kuma Jigawa.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!