Connect with us

Kiwon Lafiya

Shuba Buhari zai bar Najeriya don fara ziyarar kwanaki goma a kasar Burtaniya

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai bar gida Najeriya a yau Alhamis domin fara wata ziyarar kwanaki goma a kasar Burtaniya.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin yadda labarai, Femi Adesina.

Sanawar ta ce shugaba Buhari zai tafi Burtaniya ne bayan ya dawo daga wata ziyara da zai kai yau a garin Maidugurin jihar Borno.

A cewar Femi Adesina ta cikin sanarwar dai, shugaba Buhari zai dawo gida Najeriya daga ziyarar da zai kai Burtaniya a ranar biyar ga watan gobe na Mayu.

A jiya Juma’a ne dai shugaba Buhari ya kai ziyara Lagos, inda ya kadadamar da wasu muhimman ayyukan da gwamnan jihar Lagos Akinwumi Ambode

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!