Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu ya naɗa Gbajabiamila shugaban kwamitin kafa yan sandan jihohi

Published

on

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya naɗa shugaban ma’aikatan fadarsa Femi Gbajabiamila, a matsayin shugaban kwamitin kafa ‘yan sandan jihohi.

 

Wannan na cikin wata sanarwa da mai ba shugaban ƙasar shawara kan harkokin yaɗa labarai Bayo Onanuga, ya fitar, yana mai cewa, babban  Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi shi mamba ne a kwamitin.

 

Ta cikin sanarwar, Onanuga ya ce an kafa wannan kwamiti ne domin shirya tsarin doka da zai ba da damar aiwatar da tsarin kafa ‘yan sandan jihohi a faɗin Najeriya.

 

Shugaba Tinubu, wanda Gbajabiamila ya wakilta a wajen ƙaddamar da kwamitin a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, ya bayyana cewa kafa kwamitin ya zama wajibi ne bayan Majalisar Dokoki ta Ƙasa ta amince da Kudirin Gyaran Kundin Tsarin Mulki na shekarar 2026 da ya tanadi kafa ‘yan sandan jihohi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!