Labarai
SDP ta soki Tinubu kan naɗa Gbajabiamila shugaban kwamitin tsara dokar kafa yan sandan jihohi

Jam’iyyar SDP ta soki matakin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na naɗa Shugaban Ma’aikatansa, Femi Gbajabiamila, a matsayin shugaban kwamitin da zai tsara dokar aiwatar da kafa yan sandan jihohi.
Shugaban SDP na ƙasa, Farfesa Sadiq Gombe, ya ce bai dace Gbajabiamila ya ci gaba da riƙe wannan muƙami ba, kasancewar ana binciken wasu zarge-zarge da ake masa.
Ya ce ya kamata ya ajiye muƙaminsa har sai an kammala binciken domin tabbatar da gaskiya.
Sai dai Fadar Shugaban Ƙasa ta musanta zarge-zargen da ake yi wa Gbajabiamila, yayin da Shugaba Tinubu ya bayyana cewa yana da cikakken yaƙini da amincinsa, tare da ci gaba da ba shi goyon baya.
You must be logged in to post a comment Login