Connect with us

Ƙetare

Shugaba Trump zai ƙarfafa dokokin zaɓe a Amurka

Published

on

Shugaban Amurka Trump ya ce zai kauce wa Majalisar Dokoki tare da tilasta sabbin dokoki masu tsauri na tantance masu kaɗa ƙuri’a kafin zaɓen tsakiyar wa’adi na watan Nuwamba.

Majalisar ta amince da wani ƙudiri da ke buƙatar masu son kaɗa ƙuri’a su gabatar da shaidar zama ƴan ƙasa, amma da wuya ya samu karɓuwa a Majalisar Dattawa.

Mista Trump bai yi bayanin yadda zai sanya irin waɗannan dokoki ba, waɗanda masu suka ke cewa za su hana miliyoyin masu kaɗa ƙuri’a shiga zaɓen.

Sai dai ya sha iƙirarin cewa magudin zaɓe ya zama ruwan dare a Amurka, ba tare da gabatar da wata shaida ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!