Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Mun baza jami’ai 200 domin cafke masu sayan kuri’a yayin zabe- EFCC

Published

on

Hukumar yaki da cin hanci da rashwa ta EFCC ta ce, ta tura jami’anta 200 zuwa jihohin Kano da Jigawa da Katsina domin yaki da masu sayen kuri’u yayin zaben gwamna da ‘yan majalisar dokoki da za a gudanar ranar Asabar mai zuwa.

Shugaban hukumar ta EFCC shiyyar Kano Farouk Dogondaji ne ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da manema labarai da safiyar yau Alhamis.

Ya ce, sun tura jami’ai hamsin domin sanya ido kan yadda zaben zai gudana a jihar Kano, sai wasu jami’ai hamsin su ma a jihar Jigawa, yayin da aka tura wasu jami’ai hansin jihar Katsina domin hana sayen kuri’u a lokacin zaben.

A cewarsa sauran jami’an an tura su zuwa filin jirgin saman Malam Aminu Kano da kuma filin jirgin saman Umaru Musa Yar’adua da ke Katsina.

Farouk Dogondaji ya kuma ce, tura jami’an na daga cikin kudirin hukumar EFCC na tabbatar da sahihin zabe.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!