Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Ƙetare

Shugaba William Ruto ya bukaci kasashe Afrika masu karfin masana’antu su samar da  karin fasahohi

Published

on

 

Shugaban kasar Kenya William Ruto, ya ce, ya kamata manyan kasashe masu karfin masana’antu, su samar da kudi da fasahohin da ake bukata wajen taimakawa kasashen Afrika domin shawo kan matsalolin da sauyin yanayi ke haifarwa.

Da yake jawabi yayin taron makon tattauna muhimman batutuwan nahiyar Afrika na bana, wanda ake kira da Ibrahim Governance Weekend, da ke gudana yanzu haka a Nairobi babban birnin kasar ta Kenya, Shugaba William Ruto, ya jaddada cewa manyan kasashe na da nauyin da ya rataya a wuyansu na tabbatar da adalci wajen shawo kan sauyin yanayi a Afrika.

Haka kuma ya kara da cewa, karuwar yanayin zafi ne ke yin matukar tasiri a kan muhalli da rayuwar jama’a.

Ya kara da cewa nahiyar Afrika na bukatar diyyar asarar da ta tafka saboda matsalolin da sauyin yanayi ya haifar kan tattalin arzikinta.

Shugaban kasar ta Kenya, ya ce, ya kamata a taimaka wa Afrika wajen sake farfado da tsarin kiyaye muhalli, yana mai cewa, Kenya za ta karbi bakuncin taron nahiyar kan sauyin yanayi daga ranar 4 zuwa 6 ga watan Satumban bana.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!