Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu ya gana da manyan hafsoshin tsaro a fadar mulki ta Villa

Published

on

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya jagoranci wani taron tsaro a Fadar sa da ke Abuja da yammacin Alhamis din makon nan tare da manyan hafsoshin rundunonin tsaro da shugabannin hukumomin leƙen asiri.

 

Rahotonni sun bayyana cewa taron ya mayar da hankali ne kan nazarin halin tsaro a sassa daban-daban na Najeriya, da kuma duba yadda ake gudanar da ayyukan soji a yankunan da ake fama da matsalolin tsaro.

 

Sai dai majiyoyi sun tabbatar da cewa, an gudanar da taron ne a sirrance har na tsawon fiye da sa’o’i biyu.

 

Wananan dai na zuwa ne bayan da rundunar Operation FANSAN YAMMA ta sanar da dakile wani shirin hare-haren ‘yan ta’adda a jihohin Zamfara da Katsina.

 

Rundunar ta ce jiragen yaƙin sojin saman Najeriya sun kai hare-hare kan ayarin ‘yan ta’adda da ke kan babura, tare da kashe wani fitaccen shugaban ‘yan bindiga mai suna Alhaji Tukur a yankin Dogon Kade.

 

Haka kuma, a Arewa maso Gabas, rundunar Operation Hadin Kai ta ce ta dakile wani hari da aka kai sansaninta na Mairari a jihar Borno.

Sai dai har zuwa wannan lokaci, fadar shugaban ƙasa ba ta fitar da wata sanarwa kan sakamakon taron ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!