Labarai
Sojoji sun kashe jagoran yan ta’adda a Kogi

Dakarun rundunar sojin Najeriya, sun kashe wani jagoran yan ta’adda a Jihar Kogi, bayan wani farmaki da suka kai a dajin Adankolo da ke Lokoja.
A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Laftanar Hassan Abdullahi, ya fitar ranar Lahadi, ya ce, sojojin sun kai harin ne bayan samun ingantaccen bayanan sirri kan zirga-zirgar wasu da ake zargin ‘yan ta’adda ne a yankin.
Sanarwar ta ce sojojin sun yi kwanton ɓauna a hanyar da ake zargin ‘yan bindigar ke bi, inda aka yi musayar wuta. A yayin artabun, an kashe mutum guda daga cikin waɗanda ake zargi, yayin da sauran suka tsere cikin daji da raunukan harbin bindiga.
Sojojin sun kuma kwato bindigogi biyu ƙirar AK-47 da harsasai guda 145, da ababen hawa da kuma kudade da suka kai Naira N62,900.
You must be logged in to post a comment Login