Connect with us

Labarai

Sojoji sun kashe ‘ƴan ta’adda’ biyu da ceto mutum uku a Benue

Published

on

Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta na Operation Whirl Stroke tare da haɗin gwiwar jami’an tsaron al’umma na jihar Benue sun kashe wasu da ake zargin ‘yan ta’adda biyu tare da ceto mutum uku da aka yi garkuwa da su a wani samame da suka kai a ƙaramar hukumar Katsina-Ala ta jihar Benue.

A cewar sanarwar rundunar, an fara aikin ne da misalin ƙarfe 3 na safiyar ranar 16 ga Yulin 2026, inda sojojin suka bi ta Takum a jihar Taraba zuwa ƙauyukan Tse Togo da Utenge da ke kusa da sansanin Orter, inda aka ce waɗanda ake zargin ‘yan ta’addan ne ke fakewa.

“A yayin musayar wuta kuma sojojin suka samu nasarar kashe mutum biyu daga cikinsu.” in ji sanarwar.

Mutanen da aka ceto dukkaninsu mazauna ƙaramar hukumar Katsina-Ala ne in ji sanarwar.

Rundunar ta ce wasu daga cikin mutanen da aka yi garkuwa da su sun tsere daga sansanin yayin artabun.

Sojojin sun kuma ƙwato makamai da harsasai daban-daban da kayan soji yayin samamen.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!