Connect with us

Labarai

Taimaka wa manoma da gwamnatin ke shirin yi zai kawo gagarumin sauyi- AFAN

Published

on

Shugaban Kungiyar gamayyar Manoma ta Najeriya AFAN Alhaji Muhammad Magaji Gettado, ya ce, matakin da gwamnatin tarayya ke shirin dauka na tallafawa manoman rani da na damuna zai kawo gagarumin sauyi wajen wadata kasar nan da abinci a damunar bana.

Alhaji Muhammad Magaji Gettado ya bayyana hakan yayin kaddamar da shirin tallafin mai suna FarmerMoni ga shugabannin manoman jihohi talatin da shida dake kasar nan, da aka gudanar a ranar Laraba.

Alhaji Muhammad Magaji Gettado ya kara da cewa wannan wani tagomashi ne ga manoma da masu kiwon dabbobi, yayin da suke shirin tunkarar noman rani da na damuna.

Shugaban ya tabbatar da cewa kungiyar ta AFAN za ta sa ido kan tantancewar domin ganin manoma na gaskiya ne kawai zasu ci gajiyar tallafin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!