Connect with us

Labarai

Tallafin Corona: An dakatar da kwamandan Hisbah na Dala

Published

on

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta dakatar da kwamandan Hisbah na ƙaramar hukumar Dala Suyuɗi Hassan Muhammad.

Jami’in yaɗa labaran hukumar Ibrahim Lawal Fagge ne ya tabbatar da hakan ga Freedom Radio.

Fagge ya ce, babban kwamandan hukumar Hisbah na jiha ne ya dakatar da shi har tsawon wata guda.

Dakatarwar ta biyo bayan zargin salwantar da kayan tallafin Corona da aka bayar domin rabawa al’umma.

A ranar Juma’a ne aka yi zama da ɓangarorin masu ƙorafi domin kawo dai-dai-to ga me da lamarin, amma aka tashi baram-baram.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!