Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kano: Hisbah ta yi sulhu da masu gidajen kallo da wuraren shaƙatawa

Published

on

Hukumar Hisbah ta yi sulhu da masu gidajen kallo da wuraren shaƙatawa da masu ɗakunan taro na jihar Kano.

A Talatar nan ne Hisbah ta gana da shugabannin ƙungiyoyin su domin tattauna yadda za a samu daidaito a tsakani wajen gudanar da ayyukansu.

Babban Kwamandan Hisbah Malam Haruna Ibn Sina ya ce, suna fatan ganin masu gidajen kallo da wuraren shaƙatawa su sanya musulunci a cikin ayyukansu.

A cewarsa, ba gaskiya ba ne labarin da ake yaɗawa na cewa Hisbah za ta rufe gidan kallo ko wurin shaƙatawa domin ba ta da wannan hurumin.

Karin labarai:

Black Friday: An samu saɓani tsakanin Hisbah da majalisar malamai a Kano

Tallafin Corona: An dakatar da kwamandan Hisbah na Dala

Kwamandan ya ƙara da cewa, za su yi haɗin gwiwa da shugabannin ƙungiyoyin ta yadda za su riƙa aiki tare domin tabbatar da ba a keta dokokin musulunci ba.

Manyan abubuwan da Hisbah ta ja hankalin ƙungiyoyin sun haɗa da, sanya idanu kan ƙananan yara da ke zuwa wuraren, da kuma masu shaye-shayen miyagun ƙwayoyi.

Sai kuma batun zuwan ƴan mata wuraren shaƙatawa barkatai.

Da yake mayar da jawabi a madadin ƙungiyoyin Murtala Tijjani ya yaba wa hukumar ta Hisbah kan yadda ta nuna kulawa a gare su har ta gayyace su domin tattaunawa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!