Connect with us

Labarai

Tinubu ya karɓi bakuncin sabon Shugaban Jamhuriyar Benin, Wadagni

Published

on

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya karɓi sabon shugaban kasar Benin Romuald Wadagni, a gidansa da ke Ikoyi a birnin Legas ranar Litinin.

A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, wannan ita ce ganawar farko ta ƙashin kai tsakanin shugabannin biyu tun bayan rantsar da Wadagni a matsayin shugaban Benin a ranar 24 ga Mayun 2026. Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ne ya tarbi shugaban na Benin bayan isowarsa tare da raka shi zuwa gidan Tinubu.

Shugabannin biyu sun gudanar da wata ganawa ta sirri wadda ta ɗauki kusan mintuna 30, sai dai ba a bayyana cikakkun bayanan abin da suka tattauna ba. Ziyarar ta Wadagni na zuwa ne bayan nasararsa a zaɓen shugaban ƙasa da aka gudanar a Benin ranar 12 ga Afrilu, inda ya gaji tsohon shugaban ƙasar, Patrice Talon.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!