Connect with us

Ƙetare

Tinubu ya mika ragamar shugabancin ECOWAS ga Julius Maada Bio

Published

on

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya mika ragamar shugabancin ƙungiyar ECOWAS ga Shugaban kasar Saliyo, Julius Maada Bio.

 

Tinubu ya mika ragamar shugabancin ne yayin babban taron shugabannin ƙasashen yankin wanda aka gudanar ranar Lahadi a birnin tarayya Abuja.

 

Shugaba Tinubu ya jagoranci ƙungiyar ta ECOWAS na tsawon shekaru biyu, tun daga watan Yuli na shekara ta 2023, kuma ya kammala wa’adin nasa a taron koli na 67 da aka gudanar a birnin tarayya Abuja.

 

Shugaba Tinubu, ya ce, ya na da kwarin gwiwa cewa yankin zai ci gaba da tafiya kan turbar zaman lafiya da kwanciyar hankali da kuma ci gaban tattalin arziki.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!