Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Mesut Ozil: Ko Mikel Arteta zai sabonta kwantiragin dan wasan?

Published

on

Yanzu haka dai kwantiragin Ozil a Arsenal zai kare ne a watan farkon na kakar wasa mai zuwa ta 2021.

Rashin tabuka abin a zo a gani da kungiyar kwallon kafa ta Arsenal ke fama dashi a wannan lokacin, ya sanya alamar tambaya ga matakin da Mikel Arteta ya dauka na cigaba da ajiye dan wasa Mesut Ozil a kan benci.

Tun dai a watan Maris da Arsenal ta yi nasara da ci 1 da nema kan West Ham United, rabon da Ozil ya taka wasa a kungiyar.

Arteta ya dauki matakin cire dan wasan daga tawagar ‘yan wasa 25 da zasu fafata a gasar firimiya da kuma Europa League a watan Oktoba da ya gabata.

Ozil dai ya ce, ko kadan bashi da aniyar barin kungiyar har sai lokacin da kwantiragin sa ya kare a karshen wannan kakar wasanni da muke ciki.

Arsenal tasha kungiya a wannan lokacin inda ta samu cin kwallo 10 a wasanni 11 kuma ta dawo mataki na 15 a kan tebirin gasar firimiya ta kasar Ingila.

Tsohon jami’in wucin gadi da ya rike Arsenal a shekarar 2019 bayan an kori Unai Emery, Freddie Ljungberg ya saka Ozil a cikin nagartattun ‘yan wasa 4 a kungiyar da sukafi kowa kokari a gasar firimiya ta Ingila a kakar wasa data gabata.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!