Connect with us

Ƙetare

Trump ya soke zuwan wakilansa Islamabad domin tattaunawa da Iran

Published

on

Shugaban Amurka, Donald Trump ya tabbatar da soke bulaguron wakilansa zuwa Islamabad domin tattaunawa da wakilan Iran da nufin kawo ƙarshen yaƙin.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, Trump ya ce: “Na soke tafiyar wakilaina zuwa birnin Islamabad domin tattaunawa da wakilan Iran don kawo ƙarshen yaƙin ƙasar”.

“An ɓata lokaci mai yawa a wannan bulaguro, ana ta kwan gaba kwan baya”.

“Baya ga haka, akwai saɓani da rashin tabbas a tsakanin shugabanninsu, ba wanda ya san wa ke da iko, ciki har da su shugabannin”, in ji shi.

“Kuma mu mun shirya, amma su ba su shirya ba, idan suna buƙatar tattaunawar, sa kira mu”, a cewar Shugaba Trump.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!