Labarai
Jam’iyyar ADC ta zargi gwamnatin Tinubu da jefa mutane cikin yunwa

Jam’iyyar ADC ta zargi gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu da jefa al’ummar kasar nan cikin matsananciyar yunwa sakamakon gazawar manufofinta da kuma rashin shawo kan matsalar tsaro.
Sakataren Yaɗa Labaran jam’iyyar na ƙasa, Malam Bolaji Abdullahi, ne ya bayyana hakan ta cikin sanarwar da ya fitar a jiya Litinin.
Sanarwar ta bayyana cewa jam’iyyar ta yi wannan zargin ne bayan rahoton Hukumar Abinci ta Majalisar Ɗinkin Duniya, WFP, wanda ya nuna cewa mutane sama da miliyan 17 a jihohin Arewa tara na fama da matsananciyar yunwa.
ADC ta ce hare-haren ‘yan bindiga da ‘yan ta’adda kan manoma, da tsadar rayuwa, sun ƙara ta’azzara matsalar.
Sanarwar ta ce gwamnatin Tinubu ta gaza kare rayuka da dukiyoyin manoma, tana mai cewa matsalar yunwar da ake fama da ita ba ta samo asali daga ibtilaʼi ba, illa sakamakon gazawar gwamnati.
Jam’iyyar ta kuma bayyana cewa idan ta samu damar mulki za ta bai wa noma da samar da wadataccen abinci fifiko, tare da aiwatar da manufofin da za su ƙara yawan amfanin gona da rage tsadar abinci a faɗin ƙasar.
You must be logged in to post a comment Login