Connect with us

Labarai

Ayyukan ƴan bindiga ya tilasta wa fiye da mutane 16,000 barin muhallanssu a tafkin Tchadi- OCHA

Published

on

Hukumar kula da ayyukan jinkai ta Majalisar Dinkin Duniya OCHA ta ce tashin hankali mai nasaba da ayyukan ƴan bindiga ya tilasta wa mutum sama da dubu 16 barin muhallanssu a tafkin Tchadi daga watan Janairu zuwa Maris shekara 2026.

A rahoton da ta fitar, ta ce duk da an samu ragowar ayyukan ƴan bindiga idan aka ƙwatanta da shekara bara ƴan bindigar sun kashe mutum 22 sannan sun jikkata wasu  36 yayin da su ka yi awon gaba da mutum 109 a hare-hare  63 da suka kai a watanni ukun farko na wannan shekara.

Yankunan da lamarin yafi kamari sun hada da Wadi Hawar da Wadi Fira da Tama da Kobe sai kuma yankin Ouaddai da ke gabashin ƙasar.

Rahotanni su ce a yayin da damuna ta fara kankama sannan yanayin tsaro ke kara ta’azzara yan gudun hijra na cigaba da kwarara zuwa yankunan abin da ke barazanar haifar da karancin abinci da ababen more rayuwa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!