Connect with us

Labarai

Tsofaffin Sojoji sun gudanar da zanga-zanga a Abuja

Published

on

Wasu tsoffin Sojojin kasar nan, sun gudanar da zanga-zanga a birnin tarayya Abuja, bayan da jami’an tsaro suka hanasu shiga harabar Ma’aikatar Tsaro domin neman a aiwatar da karin kudi a fanshon su.

 

Rahotonni sun bayyana cewa, tsoffin sojojin sun taru a wani fili da ke kusa da ma’aikatar da tsakar ranar yau Laraba dauke da kwalaye masu rubuce-rubuce da ke bayyana bukatunsu.

 

Sai dai, yayin da suke kokarin isa babbar kofar ma’aikatar, sai sojoji suka hana su shiga.

 

Jami’an ’yan sanda da na Hukumar tsaro ta Civil Defence ma sun bada gudunmawar tare hanyoyin da suke kusa da ma’aikatar.

 

Amma daga bisani, tsoffin sojojin suka koma tsakiyar hanya, inda suka yi wa manema labarai bayani kan korafinsu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!