Connect with us

Labarai

Iyalan tsoffin Yan sanda sun yi zanga-zanga kan rushe musu muhallai a Sokoto

Published

on

Wasu iyalan jami’an ’yan sanda sun gudanar da zanga-zanga a Sokoto, bayan da aka rushe wasu gidajensu da ke kan titin Kontagora.

 

Guda cikin matayen da aka sakaye sunanta ta ce rushewar ta yi wa iyalan jami’an da suka sadaukar da rayukansu wajen kare kasa rashin adalci, inda ta nemi hukumomin ’yan sanda su shiga tsakani.

 

Sai dai Kwamishinan Filaye da Gidaje na jihar, Nasiru Dantsoho, ya ce bai da masaniya kan rushewar, yana mai cewa batun yana gaban kotu.

 

Rahotanni sun ce kotu ta umurci wadanda abin ya shafa da su bayyana gabanta ranar Talata, 8 ga Satumba, 2026.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!