Connect with us

Kasuwanci

TUC ta bai wa gwamnati kwanaki 14 kan ta janye yunkurinta na karin kudin Mai

Published

on

Ƙungiyar ƙwadago ta TUC ta yi watsi da matakin gwamnatin tarayya na ƙara kaso 5 cikin 100 kan farashin kowacce litar mai, ta na mai kwatanta hakan a matsayin ganganci ga tattalin arzikin ƙasa.

 

A cewar gwamnatin tarayyar ta ɗauki wannan mataki ne don samun kuɗaɗen shiga da za’a yi amfani da su wajen gina hanyoyi da sauran manyan ayyuka a ƙasar nan.

 

Tuni dai ƙungiyar ta bai wa gwamnatin wa’adin kwanaki 14  da ta janye wannan matakin, ko kuma ta ɗauki matakin da take ganin ya dace.

 

A cewarta cikin matakin da zata ɗauka har da rufe manyan sassan gwamnati musamman masu samar da kuɗaɗen shiga.

 

Ta cikin wata sanarwa da Festus Osifo da kuma Nuhu Toro shugabannin ƙungiyar suka sanyawa hannu, sun ce a halin da ake ciki ƴan Najeriya na cikin ƙangin biyan haraje-haraje barkatai.

 

Shugabannin ƙungiyar ƙwadagon, sun ce sabon harajin ba abu ne da zai yiwu ba, don haka ya zama wajibi gwamnati ta dakatar da shi.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!