Connect with us

Labaran Wasanni

Victor Osimhen ba zai bugawa Najeriya gasar cin kofin Afrika ba

Published

on

Dan wasan kungiyar kwallon kafa ta Najeriya Super Eagles dake wasa a Napoli dake kasar Italiya Victor Osimhen, ba zai bugawa Najeriya gasar cin kofin kasashen Afrika ba da za a buga a shekara ta 2022.

Rahotanni daga ƙasar Italiya a tawagar sa ta Napoli , sun tabbatar dacewar dan wasan zai shafe tsawon watanni 3 yana jinya, da hakan ya sa ba zai samu damar buga gasar ba.

Dan wasan ya samu rauni a ranar lahadi 21 ga watan Nuwambar shekara 2021 a wasan da ƙungiyar sa ta yi da Inter Milan a gasar Seria A ta kasar Italiya.

Tuni dai an yiwa ɗan wasan Tiyata , na raunin da ya samu a kafar sa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!