Connect with us

Labarai

Sarkin Musulmi ya musanta rahoton goyon bayan sake zaɓar shugaba Tinubu a 2027

Published

on

Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, ya musanta rahoton da ke cewa ya bayyana goyon baya ga sake zaɓen Shugaba Bola Ahmed Tinubu a shekarar 2027.

 

Haka na kunshe cikin sanarwar da Prince Bashir Adefaka ya fitar a madadin Sashen Yaɗa Labaran Masarautar a daren jiya Talata.

 

Sanarwar ta bayyana cewa ba zai yiwu Sarkin Musulmi ya yi irin wannan furuci ba, domin a matsayinsa na uba ga kowa ba ya nuna bambanci tsakanin ‘yan siyasa ko jam’iyyun siyasa.

 

Sanarwar ta ƙara da cewa Sarkin Musulmi na ci gaba da karɓar duk masu neman shawararsa da addu’arsa ba tare da la’akari da jam’iyyarsu ba, tare da buƙatar al’umma su yi watsi da rahoton da ke danganta shi da goyon bayan kowane ɗan takara.

 

Haka kuma sanarwar ta yi kira ga kafafen yaɗa labarai da masu amfani da kafafen sada zumunta da su tabbatar da sahihancin bayanai kafin yaɗa su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!