Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

World Cup Qualify 2022: Najeriya ta doke kasar Cape Verde da ci 2-1

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Kasa Super Eagles ta doke kasar Cape Verde da ci 2-1 a wasan neman tikitin buga kofin Duniya da za a gudanar a shekarar 2022 a kasar Qatar.

Wasan da aka buga a babban filin wasa na Estádio Municipal Adérito Sena, dake yankin Mindelo a kasar ta Cape Verde.

Nasarar da Najeriya ta samu a yau Talata 7 ga Satumbar shekarar 2021 ya bata damar darewa zuwa mataki na 1 da maki 6 a rukunin da take na C.

Najeriya dai ta warware kwallon da aka zura mata ta hannun dan wasan gaban ta dake wasa a kungiyar kwallon kafar Napoli dake kasar Italiya Victor Osimhen, bayan samun tai mako daga hannun dan wasa Jamilu Collins a minti na 30.

Tunda da fari dai dan wasan kasar Cape Verde Dylain Tavares ne ya zurawa Najeriya kwallo a minti na 19 da fara wasan.

Sai dai mintina kadan a kammala wasan Kenny Santos ya zura kwallo a ragar kasarsa wato Own goal a minti na 77 da hakan ya bawa Najeriya nasara.

Da sakamakon ne Najeriya ke a mataki na 1 a rukinin da take na C da maki 6, inda Liberia ke biye mata a matsayin ta 2 da maki 3 sai kasar Cape Verde da Afrika ta tsakiya dake da maki 1 kowannan su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!