Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Yan wasan Najeriya 9 ba za su buga wasan Cape Verde ba -Rohr

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta kasa Super Eagles za ta buga wasan neman tikitin buga kofin Duniya da kasar Cape Verde ba tare da ‘yan wasan ta guda 9 ba.

Najeriya dai za ta buga wasan na ta ne a ranar Talata 7 ga Satumbar 2021.

Mai horar da kungiyar Gernot Rohr ne ya tabbatar da hakan a taron manema labarai da ya gudanar gabannin wasan.

Qatar 2022: Gernot Rohr ya fitar da sunayen ‘yan wasa 30 a wasan Liberia da Cape Verde

Hukumar kwallon kafa ta kasar Ingila ce ta haramtawa ‘yan wasan da ke wasa a kasar buga wasa a wasu kasashen da Ingila ta nuna kin gamsuwar ta sakamakon tsoran kamuwa da cutar Covid- 19 wadda kasar Cape Verde na cikin kasashen.

Sai dai mai horarwa Gernat Rohr bai ambaci ko sunayen wadanne ‘yan wasa bane, inda tuni ‘yan wasa 5 cikin 9 da ke buga wasa a kasar ingila suka bar sansanin Super Eagles bayan tashi daga karawa da kasar Liberia.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!