Labarai
Ya sanda sun kashe yan bindiga 2 tare da kubutar da wadanda aka sace

Rundunar ‘yan sandan Babban Birnin Tarayya Abuja ta sanar da kashe wasu ‘yan bindiga biyu da ke addabar al’ummomin yankin Abuja, yayin da aka ceto mutane biyar da aka sace a kauyen Paze da ke gundumar Byazhin a karamar hukumar Bwari.
Kwamishinan ‘Yan Sandan a birnin, CP Ahmed Mohammed Sanusi, ya ce shi ne ya jagoranci farmakin hadin gwiwa da jami’an sashen yaki da garkuwa da mutane, rundunar IRT, Kubwa Area Command, tare da mafarauta da ‘yan banga suka gudanar a daren Talata. A cewarsa, an kama wasu mutane biyu da ake zargi, Icheh Mohammadu da Abubakar Usman, yayin da sauran ‘yan kungiyar suka tsere zuwa tsaunuka da ke kusa.
An kuma kwato bindigogi kirar AK-47 guda biyu tare da mujallu. Mutanen biyar da aka ceto an kai su asibiti domin duba lafiyarsu kafin a mayar da su hannun iyalansu. Rundunar ta ce tana ci gaba da farautar sauran wadanda suka tsere tare da kira ga asibitoci da jama’a su kai rahoton duk wanda ya nemi maganin raunin harbin bindiga cikin yanayi mai tayar da hankali.
You must be logged in to post a comment Login