Connect with us

Labarai

Yan sandan sun cafke mutane 4 tare da kashe wasu biyu bisa zarginsu da hannu a sace kanwar tsohon Adelabu

Published

on

Rundunar ’yan sandan Jihar Oyo ta tabbatar da cafke mutane hudu tare da kashe wasu biyu  a yankin Ayegun da ke karamar hukumar Oluyole a Ibadan, da ake zargi da hannu a sace kanwar tsohon Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu, mai suna Busola, tare da ’ya’yanta biyu.

 

Kwamishinan ’yan sandan jihar, Oluwagbemiga Abimbola, ya ce jami’ansu sun samu bayanan sirri ne wanda ya kai su maboyar masu garkuwar, inda suka ceto wadanda aka sace bayan shafe sa’o’i suna gudanar da aiki. 

 

Ya kara da cewa an kwato makamai daban-daban ciki har da bindigar pump-action a wurin.

 

An sace Busola da tagwayen ’ya’yanta masu shekaru 12 a safiyar Laraba a yankin Elewura-Challenge na Ibadan a makon da ya gabata. 

 

Wannan dai na zuwa ne yayin da ake cigaba da kiraye-kirayen ceato dalibai da malamai da aka sace a jihar ta Oyo a baya bayan nan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!