Labarai
Ya zama wajibi a kawo ƙarshen barazanar tsaro ga dalibai – Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2021/09/NHRC.jpeg)
Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta kasa NHRC ta buƙaci gwamnatin tarayya da ta ɗauki matakan kare dalibai daga barazanar tsaro.
Shugaban ƙungiyar Tony Ojukwu ne ya bayyana hakan a Abuja, gabanin babban taron da ƙungiyar za ta gudanar karo na 4 a ƙasar nan.
Tony Ojukwu ya ce, kai wa makarantu hari tare da kashe dalibai ko sace su babbar barazana ce da za ta haifar da koma baya a bangaren ilimi.
Har ma ya bayyana cewa, taron ƙungiyar na bana zai mayar da hankali kan tattauna batun ƙalubalen tsaro a harkar ilimi, don samar da mafita mai kyau ga yara masu tasowa.
You must be logged in to post a comment Login