Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ya zama wajibi a kawo ƙarshen barazanar tsaro ga dalibai – Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta kasa NHRC ta buƙaci gwamnatin tarayya da ta ɗauki matakan kare dalibai daga barazanar tsaro.

Shugaban ƙungiyar Tony Ojukwu ne ya bayyana hakan a Abuja, gabanin babban taron da ƙungiyar za ta gudanar karo na 4 a ƙasar nan.

Tony Ojukwu ya ce, kai wa makarantu hari tare da kashe dalibai ko sace su babbar barazana ce da za ta haifar da koma baya a bangaren ilimi.

Har ma ya bayyana cewa, taron ƙungiyar na bana zai mayar da hankali kan tattauna batun ƙalubalen tsaro a harkar ilimi, don samar da mafita mai kyau ga yara masu tasowa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!