Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

‘Yan bindiga sun kashe sojoji 9 na rundunar Operation Cat Race a Kaduna

Published

on

‘Yan bindiga sun kashe wasu sojoji Tara da ke cikin rundunar dakarun Operation Cat Race a yankin karamar hukumar Birnin Gwari da ke jihar Kaduna.

Rahotanni sun ce ‘yan bindigar sun kai harin ramuwar gayya ne sakamakon kisan gillar da sojoji suka yiwa shugaban su a kwanakin baya mai suna Buhari wanda aka fi sani da Buharin Daji.

Jami’an tsaro ne dai suka kashe Buharin Daji yayin wani ba ta kashi da suka yi a jihar Zamfara makwanni biyu da suka wuce.

Sai dai har zuwa yanzu rundunar sojin kasar nan ba ta fitar da sanarwa kan batun ba, yayin da ana sa bangaren gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai, ya mika da sakon ta’aziya ga iyaye da kuma ‘yan uwa da abokan arzikin mamatan.

Wata majiya ta shaidawa manema labarai cewa ‘yan bindigar sun kai harin ne da misalin karfe takwas zuwa tara a kauyen Kampani da ke yankin karamar hukumar Birnin Gwari.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!