Connect with us

Labarai

’Yan Boko Haram sun kai hari kan ayarin ɗan takarar gwamnan jihar Borno

Published

on

Rundunar ’yan sandan Jihar Borno ta tabbatar da cewa ’yan Boko Haram sun kai hari kan ayarin ɗan takarar gwamnan jihar na jam’iyyar APC, Injiniya Mustapha Gubio.

 

Kakakin rundunar, ASP Keneth Daso, ya ce harin ya faru ne a kan hanyar Gubio zuwa Kareto da Damasak, a arewacin jihar, yayin da ayarin ke kan hanyarsa daga Damasak zuwa Maiduguri.

 

Ya ce ’yan ta’addan sun yi wa ayarin kwanton bauna tare da dasa bama-baman IED da kuma harba rokoki, amma jami’an tsaro da suka haɗa da ’yan sanda, sojoji, NSCDC, DSS da ’yan banga sun dakile harin.

 

A cewar ASP Daso, babu asarar rai daga ɓangaren jami’an tsaro ko fararen hula.

 

Sai dai majiyoyi sun shaida wa wakilinmu cewa wata motar sulke ta ’yan sanda da ke cikin ayarin ta samu lahani yayin arangamar.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!