Labarai
INEC za ta fitar da sunayen karshe na ƴan takarar shugaban kasa

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC, ta shirya fitar da jerin sunayen karshe na ƴan takarar shugaban kasa da majalisar kasa da za su fafata a zaben 2027, a ranar Asabar 12 ga Satumba, 2026.
Zaben shugaban kasa da na majalisar kasa dai an tsara gudanar da su ne a ranar 16 ga Janairu, 2027.
Jerin zai kunshi ƴan takarar shugaban kasa da mataimakansu, da kuma wadanda ke neman kujerun majalisar Dattawa 109 da ta Wakilai 360, wato kujeru 469 gaba daya ke nan.
INEC ta ce matakin na cikin jadawalin shirye-shiryen zaɓen, kuma ya yi daidai da tanadin dokar zabe ta 2026, wadda ta tanadi fitar da jerin sunayen karshe akalla kwanaki 60 kafin ranar zabe.
To tuni dai hukumar ta wallafa bayanan ƴan takarar Shugaban Ƙasa domin bai wa jama’a damar duba su tare da gabatar da ƙorafe-ƙorafe kafin kammala jerin sunayen.
You must be logged in to post a comment Login