Connect with us

Labarai

Sokoto – Mutane 5 sun mutu sakamakon harin ‘Yan-bindiga

Published

on

Rundunar ’yan sandan Jihar Sokoto ta tabbatar da mutuwar mutane biyar, yayin da wasu uku suka jikkata sakamakon harin ’yan bindiga a ƙaramar hukumar Kebbe.

Harin ya faru ne a yammacin Alhamis a garin Girkau da wasu ƙauyukan da ke yankin, inda mazauna suka ce an kuma yi garkuwa da wasu mutane tare da sace dabbobi.

Kakakin rundunar, DSP Ahmed Rufai, ya ce har yanzu suna tattara bayanai kan adadin mutanen da aka yi garkuwa da su.

Wani mazaunin yankin ya ce maharan sun kai hari ƙauyukan Dukura da Jibga, inda aka kashe mutum ɗaya a kowane wuri, tare da yin garkuwa da wasu mazauna yankin.

Rundunar ’yan sandan ta ce jami’an tsaro na ci gaba da ƙoƙarin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!