Labarai
Yan sanda a Jihar Rivers sun kama masu garkuwa da mutane

‘Yan sanda a Jihar Rivers sun kama wasu manyan masu garkuwa da mutan guda uku tare da ceto wasu da aka sace. An kama su ne yayin da suke ƙoƙarin sace wani mutum da suka yaudara daga Jihar Anambra da sunan za su ba shi aikin gyaran ciki (interior decoration). Rundunar ta bayyana cewa wannan nasara na daga cikin kokarin da suke yi na dakile laifuka a jihar.
Bincike ya nuna cewa waɗannan masu laifin suna amfani da kafafen sada zumunta kamar WhatsApp, Facebook, X da Tinder wajen yaudarar mutane. Suna amfani da hotunan manyan mutane domin samun amincewa daga wurin waɗanda suke son yaudara, sannan su jawo su zuwa jihar kafin su yi garkuwa da su.
Wadanda aka kama sun amsa laifukan da suka hada da wasu sace-sacen mutane a baya, yayin da jagoran kungiyar ya tsere. Rundunar ‘yan sanda ta shawarci jama’a da su rika yin taka-tsantsan da mutane da ba su sani ba a intanet, su tabbatar da sahihancin duk wata tayin aiki, kuma su sanar da ‘yan uwa kafin su hadu da sabbin mutane.
You must be logged in to post a comment Login