Connect with us

Labaran Kano

Yanzu-Yanzu: Abdulmumin Kofa ya fice daga APC

Published

on

Tsohon dan majalisar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Kiru da Bebeji a zauren majalisar tarayya Abdulmumin Jibrin Kofa ya sanar da ficewa daga jami’iyyar APC mai mulkin kasa.

Kofa ya bayyana haka ne a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook a ranar Asabar cewa

“Nayi wa APC iya kokari na lokaci yayi da zan yi gaba. Zan sanar da sabuwar jamiyyar da zan shiga cikin sa’oi 24 In sha Allah. Zanyi cikakken bayani bada jimawa ba. Hon Abdulmumin Jibrin”

Wannan dai na zuwa ne bayan da zaben shekarar 2023 ke ci gaba da karatowa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!