Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Addini

Yanzu-yanzu: Malam Abduljabbar ya nemi afuwa, kwana guda bayan muƙabala

Published

on

Malamin nan Sheikh Abduljabbar Nasir Kabara, ya nemi afuwa kan kalaman sa game da wasu hadisai da ya bayyana cewa, an ci zarafin manzon tsira Annabi (s.a.w).

A cikin wani jawabi da ya fitar da tsakar ranar Lahadi, ya ce, idan har waɗannan kalamai daga shi ne, to ba shi da wata mafita sai gaggawar neman afuwa tare da gafarar al’umma.

Ya ci gaba da cewa, idan kuma daga cikin litattafan da ya faɗa ne, to malamai su ji tsoron Allah a taru a yi yaƙi da su.

Malamin ya kuma yi ƙarin bayani kan abin da yake nufi da babu lokaci a yayin zaman muƙabala.
Ku saurari jawabin nasa a na.

https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2021/07/Jawabin-Malam-Abduljabbar-Kabara-11-07-2021.mp3?_=1

Wannan dai na zuwa ne, kwana guda bayan da aka yi zaman muƙabala tsakaninsa da malaman Kano, wanda alƙalin muƙabalar ya bayyana cewa, malamin bai amsa dukkan tambayoyin da aka masa ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!