Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kasuwanci

Yiwa kananan ‘yan kasuwa rijista zai bunkasa kasuwancin su-CAC

Published

on

Hukumar yiwa kamfanoni Rijista ta kasa (CAC) ta ce yin rijistar kasuwanci ga kananan ‘yan kasuwa zai sa kasuwancin su ya inganta tare da samun riba mai yawa.

Babban magatakarda a hukumar ta Corporate Affairs Commission wato (CAC), Alhaji Garba Abubakar ne ya bayyana hakan ya yin taron tattaunawa da masu ruwa da tsaki a hukumar.

Garba Abubakar ya kuma ce yin rijistar ga kananan ‘yan kasuwar zai sanya banku su rinka basu rancen kudade don inganta kasuwancin su.

Wasu daga cikin masu ruwa da tsaki a hukumar da suka halarci taron sun bayyana jindadin su game da ayyukanta, musamman ta yadda ake yiwa dan kasuwa ko mai kamfani rijistar kasuwancin sa a cikin Awa guda.

A yayain taron dai an baiwa mutanan da suka halarci taron damar bayar da shawara ko shigar da korafi kan yadda za’a kara inganta aikin hukumar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!