Connect with us

Labarai

Za a ƙirga kowace ƙuri’ar da aka kaɗa a zaɓen 2027- Joash Amupitan

Published

on

Shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya INEC, Farfesa Joash Amupitan, ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa za a ƙidaya kowace ƙuri’ar da aka kaɗa kamar yadda ya ke a bisa doka a babban zaɓen shekarar 2027 da ke tafe.

 

Shugaban ya ce hukumar ta koyi darussa daga ƙalubalen da aka fuskanta a zaɓukan baya, kuma ta inganta shirye-shiryenta domin tabbatar da sahihin zaɓe mai cike da gaskiya da adalci. 

 

Amupitan ya bayyana hakan ne yayin wata ziyarar ban girma da ya kai tsohon Shugaban Ƙasa, Janar Abdulsalami Abubakar mai ritaya, inda ya yi alƙawarin cewa INEC za ta gudanar da zaɓen da zai ƙara wa ‘yan Najeriya kwarin gwiwa da amincewa da tsarin dimokuraɗiyya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!