Connect with us

Labarai

Harin Ukraine kan jirgin Ruwan Iran ya hallaka mutum 1

Published

on

Iran ta ce wani hari da Ukraine ta kai kan wani jirgin ruwanta na kasuwanci a Tekun Caspian ya haddasa fashewa da ta yi sanadin mutuwar wani ma’aikacin jirgin tare da jikkata wani.

 

Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta bayyana harin a matsayin ta’addanci da cin zarafi, tare da kiran jami’in diflomasiyyar Ukraine domin mika ƙorafi.

 

A nata ɓangaren, Shugaban Ukraine Volodymyr Zelenskyy ya ce dakarunsa sun kai hari kan wani jirgin ruwan yaƙin Rasha da wasu jiragen da ake zargin suna ɗauke da kayan soji masu alaƙa da Iran a Tekun Caspian.

 

Haka kuma ya zargi Rasha da bai wa Iran bayanan tauraron ɗan adam domin taimaka mata wajen kai hare-hare a Gabas ta Tsakiya. Reuters ta ce har yanzu Ukraine ba ta fitar da wata sanarwa kai tsaye kan zargin Iran ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!