Labarai
Yan majalisar wakilai na ADC sun bukaci a sauke tare da gurfanar Farfesa Joash Amupitan

’Yan majalisar wakilai na jam’iyyar hadaka ta ADC sun bukaci a gurfanar tare da cire shugaban hukumar zabe ta kasa INEC, Farfesa Joash Amupitan, bisa zargin nuna bangaranci kafin zaben 2027.
Sun bayyana haka ne bayan taronsu na farko, inda suka ce zarge-zargen da ake yi wa shugaban hukumar, musamman batun wani asusun X da ake dangantawa da shi, na iya lalata amincewar jama’a da tsarin zabe, duk da cewa INEC ta musanta alakar sa da asusun.
’Yan majalisar sun kuma zargi hukumar da katsalandan a rikicin cikin gida na jam’iyyar, tare da gargadin cewa irin wadannan matakai na iya kawo cikas ga dimokuradiyya, suna mai kira ga a gudanar da bincike domin kare sahihancin zabe a Najeriya.
You must be logged in to post a comment Login