Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Za’a gudanar da zaben shugaban hukumar wasannin rundunar soji ta Afrika  

Published

on

Mataimakin daraktan wasanni a shalkwatar tsaro ta kasa, Brigadier Janar Maikano Abdullahi, na daya daga cikin ‘yan takarar dake neman kujerar shugabancin hukumar wasannin rundunar soji ta Afrika wato OSMA.

Manyan jami’an soji 4 ne daga kasashen Afrika da suka hadar da Najeriya da Algeria da Kenya da kuma Guinea Conakry ke takarar neman a zabe su don shugabancin hukumar.

Haka kuma, kasashe 51 wadanda mambobi ne na Afrika kawai ke da alhakin zaben wanda zai jagoranci hukumar ta OSMA.

Za dai a gudanar da zaben ne a babban taron hukumar a ranar 7 ga watan Oktoba mai zuwa ta hanyar amfani da kafar sadarwa ta Internet, sakamakon annobar cutar COVID-19.

Rahotonni na cewa, wanda duk ya samu damar lashe zaben a cikin ‘yan takarar, ya zama mataimakin shugaban hukumar wasannin rundunar soji ta duniya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!